Posts

Iran Ta Tabbatar da Mutuwar Khamenei Bayan Hare-Haren Amurka da Isra’ila; IRGC Ta Yi Alƙawarin Fansa

Image
An tabbatar da rasuwar Ali Khamenei, Jagoran Ƙoli na Jamhuriyar Musulunci ta Iran, wanda ya shafe fiye da shekaru talatin yana rike da madafun iko a kasar. Rasuwarsa ta zo ne a ranar farko ta hare-haren hadin gwiwa da aka kai kan muhimman wurare a Iran. Wannan lamari ya jefa kasar cikin sabon yanayi mai cike da tambayoyi kan makomar shugabanci da tasirin ta a yankin Gabas ta Tsakiya. Wane Matsayi Ya Rike? Mukamin Jagoran Ƙoli a Iran shi ne mafi girman iko a tsarin mulkin kasar. Shi ne shugaban kasa a zahiri, kwamandan rundunar sojoji, da mai ikon yanke hukunci kan manyan manufofi na kasa. Tun bayan juyin juya halin Musulunci na 1979, Iran ta taba samun Jagorori biyu kacal. Khamenei ne ya gaji Ayatollah Ruhollah Khomeini a 1989, kuma tun daga lokacin yake da tasiri kai tsaye a siyasa, tsaro da tattalin arzikin kasar. Tarihinsa A Takaitacce An haife shi a shekarar 1939 a birnin Mashhad. Ya taso a gidan addini kuma ya zama malamin Shi’a tun yana matashi. Ya shiga sahun masu ad...

Juyin Mulki Na Ci Gaba A Benin Republic, Sojoji Sun Kai Hari Gidan Shugaba Talon, Sun Kwace Talabijin Na Ƙasa.

Image
Rikici mai tsanani ya barke a safiyar Lahadi, 7 ga Disamba 2025, a ƙasar Benin Republic bayan rahotanni sun tabbatar da cewa wani rukuni na sojoji ya kai hari gidan shugaban ƙasar, Patrice Talon, da ke unguwar Le Guézo a Cotonou. Wani fitaccen gidan labarai na yankin, TchadOne, ya bayar da rahoton cewa harin ya samu jagoranci ne daga Lieutenant Colonel Pascal Tigri, wanda ake zargin shi ke jagorantar yunkurin hambarar da gwamnatin Talon. Bayan harin, sojoji sun mamaye gidan talabijin na ƙasa. Daga bisani, Lt. Col. Tigri ya bayyana kai tsaye a talabijin yana ayyana kansa a matsayin: “Shugaban Kwamitin Sake Tsarin Mulki na Soji.” Halalcin Birnin Cotonou Ya Ƙara Lalacewa Mutanen Cotonou sun wayi gari cikin tashin hankali saboda: Sojoji sun mamaye muhimman wurare An ji motsin manyan motocin yaƙi Gidan talabijin na hannun sojoji Gwamnati bata fitar da wata sanarwa ba Ba a san inda Shugaba Talon yake ba Har yanzu babu wata takamaiman magana daga gwamnatin Benin ko rundunar soji k...

Christopher Musa Ya Karɓi Rantsuwa Bayan Murabus ɗin Badaru

Image
A yau, 4 ga Disamba 2025, tsohon Chief of Defence Staff (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa (rtd.), ya karɓi rantsuwar kama aiki a matsayin sabon Ministan Tsaro na Najeriya. Wannan na zuwa ne bayan murabus da tsohon ministan tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya yi a makon da ya gabata. Mai magana da yawun Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Bayo Onanuga, ya tabbatar da nadin tare da fitar da hoton rantsuwar da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa Abuja. Sunan Janar Musa ya isa majalisar dattawa tun bayan murabus ɗin Badaru, kuma majalisar ta tabbatar da shi bayan tsauraran tambayoyi da aka yi masa na tsawon awa biyar. Janar Musa ya yi ritaya daga rundunar soja a watan Oktoba 2025 bayan kammala wa’adinsa a matsayin CDS, inda ya jagoranci rundunonin tsaro wajen yaki da ta’addanci a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma. Yana daga cikin manyan hafsoshin da suka yi fice a tarihin rundunar sojin ƙasa, kuma ya samu Colin Powell Award a shekarar 2012 saboda bajintar aiki. An haife shi a Soko...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Rahoton Juyin Mulki da Soke Bukin ’Yancin Kai

Image
Hedikwatar Tsaron Najeriya (DHQ) ta karyata rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa soke bikin cika shekaru 65 da samun ’yancin kai na ƙasar yana da nasaba da yunkurin juyin mulki. A cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labaran Rundunar, Brigediya Janar Tukur Gusau, ya fitar a ranar Asabar, DHQ ta bayyana rahoton a matsayin “karya tsantsa”, tana mai cewa manufarsa ita ce tada hankalin jama’a da haifar da rudani a cikin ƙasa. Gusau ya bayyana cewa soke bikin ya biyo bayan shirin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na halartar taro mai muhimmanci a ƙasashen waje, tare da bai wa rundunar tsaro damar mayar da hankali kan yaƙin da ta ke yi da ta’addanci, ’yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya a sassan ƙasar. Hedikwatar ta kuma ce binciken da ake yi kan wasu hafsoshin soja 16 ba shi da nasaba da wani yunkurin juyin mulki, illa dai mataki ne na cikin gida domin tabbatar da ladabi, da bin doka a rundunar soji. DHQ ta roƙi ’yan Najeriya da su guji yarda da labaran ƙarya, tana ma...

Najeriya ta Sake Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya

Image
Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya sabunta kira da ake dade ana yi cewa Najeriya ta samu ɗaya daga cikin kujerun dindindin guda biyu da ake shirin warewa ga Afirka a Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya (UNSC). Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a zaman Majalisar a New York, ya bayyana cewa dole ne duniya ta sabunta tsarin ta, ta yadda zai dace da yanayin zamani. A cewarsa, lokacin da aka kafa MDD a 1945, Najeriya ba ta ma kai matsayin kasa mai cin gashin kanta ba, amma yanzu ta zama kasa mai karfin tattalin arziki da yawan al’umma sama da miliyan 236. Ya jaddada cewa Najeriya ta shafe shekaru tana taka rawar gani wajen samar da zaman lafiya a duniya — tun daga Congo a shekarar 1960 zuwa Liberia, Saliyo, Sudan da sauran wurare. Haka kuma, ta taka rawa wajen kawo ƙarshen mulkin wariyar launin fata a Afirka ta Kudu. Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya yanzu haka na da mambobi 15, ciki har da mambobi biyar na dindindin (Amurka, Birtaniya, Fara...

NATO Ta Tare Jiragen Rasha da Suka Keta Samaniyar Estonia

Hukumomin Estonia sun tabbatar da cewa jiragen yaki guda uku na Rasha, nau’in MiG-31, sun keta samaniyar kasar a ranar 19 ga Satumba 2025. Rahotanni sun bayyana cewa jiragen sun shiga ne ba tare da flight plan ba, sun kashe transponders, kuma basu yi mu’amala da hukumomin zirga-zirgar jiragen sama na Estonia ba. Wannan ya faru ne a kusa da Tsibirin Vaindloo da ke cikin Gulf of Finland. A cewar gwamnatin Estonia, wannan ketarewa ta dauki tsawon mintuna 12, wanda ya sanya NATO ta aika da jiragen F-35 daga Italiya domin tarwatsa su. Bayan lamarin, Estonia ta kira Jakadan Rasha don nuna rashin jin dadin ta. Haka kuma, ta bukaci tattaunawa karkashin Article 4 na NATO, wanda ke bai wa kasashe memba damar gabatar da bukatar shawarwari idan akwai barazanar tsaro. Hukumomin kasar sun bayyana cewa wannan danyen aiki daga Rasha na iya kara jefa yankin cikin tashin hankali, musamman ganin yadda rikicin Ukraine ke ci gaba da rikita tsarin tsaro a Turai. GW Hausa