Zamfara: “Muna Rayuwa Kamar Bayi” Bayan Harin ‘Yan Bindiga Da Ya Kashe 2 Ya Sace Sama Da 100

A Zamfara Nijeriya mutane biyu sun rasa rayukansu yayin da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai mummunan hari a ƙauyen Gamdum Mallam, Bukkuyum LGA, Zamfara State, inda suka yi garkuwa da mata da yara sama da 100. Wannan harin ya faru ne a safiyar Asabar, 23 ga Agusta, 2025, lokacin da maharan suka mamaye yankin a kan babura da dama, suna harbe-harbe ba tare da tsari ba.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa maharan sun kasu gida biyu — rukuni ɗaya na yi wa jama’a kwanton bauna tare da yin garkuwa da mutane da dabbobi, yayin da wani rukuni ya kafa shingen hanya a babbar hanya ta Adafka, inda suka bude wuta kan masu neman tsira.

Wani mazaunin ƙauyen, Huzaifa Isa, ya ce: “Muna rayuwa kamar bayi a ƙasar mu. Harin ya nuna tamkar babu gwamnati da za ta kare mu.”

Wani dan majalisa na yankin, Hamisu Faru, ya tabbatar da lamarin ta wayar tarho, yana mai cewa: “Tun Asabar da safe an yi garkuwa da mutane fiye da 100.”

Harin bai tsaya a Gamdum Mallam kawai ba. An ruwaito cewa maharan sun shiga ƙauyukan Nasarawa Burkullum da Ruwan Rana, inda aka sake sace wasu mutane 46.

Rahoton sabuwar bincike daga SBM Intelligence ya nuna cewa Zamfara ce ta fi kowace jiha yawan garkuwa da mutane a Najeriya daga Yuli 2024 zuwa Yuni 2025 — inda aka sace mutane 1,203. Sai Kaduna (629), Katsina (566), da Sokoto (358).

Rahoton ya kuma bayyana cewa masu garkuwa sun nemi kudaden fansa da suka kai ₦48 biliyan, amma abin da aka biya bai wuce ₦2.56 biliyan ba. Wannan na nuna yadda matsalar ta zama babbar barazana ga tsaro da tattalin arzikin Najeriya.

Yayin da mazauna Gamdum Mallam ke shirin binne wadanda suka mutu, har yanzu daruruwan iyalai na cikin tashin hankali da kaduwa saboda yan uwansu da aka sace. Mutane na ci gaba da tambaya: Shin gwamnati za ta iya kawo karshen wannan bala’i a Zamfara da Arewa maso Yamma gaba ɗaya?

Popular posts from this blog

Juyin Mulki Na Ci Gaba A Benin Republic, Sojoji Sun Kai Hari Gidan Shugaba Talon, Sun Kwace Talabijin Na Ƙasa.

Malema Ya Nemi Shugaban Ɗaya, Kuɗi Ɗaya Da Afirka Ba Tare Da Iyaka Ba

Uganda: Zaben ‘Yan Uwa a Majalisar Dokoki Na Kara Karbuwa Al’umma Sun Mayar da Siyasa Gado?