Uganda: Zaben ‘Yan Uwa a Majalisar Dokoki Na Kara Karbuwa Al’umma Sun Mayar da Siyasa Gado?
A Uganda, zaben ‘yan uwa da ‘ya’ya na tsoffin ‘yan majalisa ya zama ruwan dare. Idan dan majalisa ya rasu, akwai yiwuwar wani daga cikin danginsa ya gaje shi—koda kuwa bai taba siyasa ba. Wannan al’ada ta kara bayyana yayin da kasar ke shirye-shiryen shiga zabukan 2026.
Misali, lokacin da Patrick Okabe, dan majalisa daga Serere County ya rasu a hadarin mota a 2022, dansa Emmanuel Omoding ya tsaya takara a zaben cike gurbi kuma ya ci. Haka zalika, lokacin da tsohon kakakin majalisa Jacob Oulanyah ya mutu a 2022, dansa Andrew Ojok Oulanyah ya maye gurbinsa. Haka kuma, Rehema Watongola ta rasu a 2020, sai diyarta Kayanga Baroda ta ci zabe da tuta mai zaman kanta.
Masana sun bayyana cewa wannan al’ada tana kara dankon ikonsa ga wasu dangogi, tana rage damar shiga sabbin shugabanni. Rogers Barigayomwe, farfesa a Jami’ar Kampala, ya bayyana hakan da cewa:
“Wannan tsarin siyasa tamkar kafa mulkin gado ne. Sai dai yana da karbuwa saboda mutane suna ganin ‘yan uwa za su ci gaba da ayyukan da wanda ya rasu ya bari.”
A Uganda, matsalar rashin wadataccen ayyuka daga gwamnati na sa mutane dogaro da yan majalisa domin samar musu da abubuwa kamar ruwan sha, asibitoci, makarantun gwamnati da kuma tallafin jama’a. Don haka, idan wani ya mutu kafin kammala ayyukan da ya dauki alkawari, jama’a na kallon dan uwansa ko diyarsa a matsayin wanda zai tabbatar da ci gaban.
Masu suka kuma na ganin wannan al’ada na taimaka wajen tsawaita ikonsa ga jam’iyya mai mulki NRM (National Resistance Movement) wadda Shugaba Yoweri Museveni ke jagoranta tsawon shekaru kusan 40. Jam’iyyar ta sha tsayar da ‘yan uwa a matsayin zababbun wakilai don ta ci gaba da rike iko a mazabun da aka rasa wakilai.
Ko da yake doka ba ta haramta hakan ba, wasu ‘yan kasa da masana na gargadi cewa siyasar gado za ta iya rage ingancin wakilci da kuma hana fitowar sababbin shugabanni. “Dimokradiyya da gaske na nufin bude hanya ga kowa,” in ji Farfesa Sabiti Makara daga Jami’ar Kabale.
Yayin da 2026 ke karatowa, ana tambaya ko Ugandawa za su ci gaba da rungumar siyasar gado, ko kuwa za su rungumi sababbin shugabanni da sabbin manufofi.